in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da babban zaben Masar a Maris mai zuwa
2018-01-09 10:55:06 cri
Jiya Litinin, kwamitin kula da harkokin zaben kasar Masar ya sanar a babban birnin kasar Alkahira cewa, za a gudanar da babban zaben shugaban kasa daga ranar 26 zuwa ranar 28 ga watan Maris mai zuwa, kuma jama'ar kasar da suke zaune a kasashen ketare za su jefa kuri'unsu daga ranar 16 zuwa ranar 18 ga watan Maris mai zuwa.

Shugaban kwamitin Lasheen Ibrahim ya bayyana a yayin taron manema labarai cewa, za a gabatar da sakamakon babban zaben shugaban kasa a ranar 2 ga watan Afrilu. Amma idan akwai bukatar gudanar da jefa kuri'u zagaye na biyu, al'ummar kasar da suke zaune a kasashen ketare za su iya jefa kuri'unsu daga ranar 19 zuwa ranar 21 ga watan Afrilu, yayin da al'ummar kasar za su jefa kuri'unsu daga ranar 24 zuwa ranar 26 ga watan Afrilu, kuma za a gabatar da sakamakon zaben a ranar 1 ga watan Mayu.

Bisa labarin da aka samu, an ce, 'yan takara za su fara yin rajista a hedkwatar kwamitin kula da harkokin zaben kasar tun daga ranar 20 zuwa ranar 29 ga watan nan da muke ciki, kuma za a gabatar da jerin sunayen 'yan takara a ranar 23 ga watan Fabrairu mai zuwa, bayan an gudanar da bincike yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China