in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana tuhumar 'yan sandan Masar da laifin safarar kudaden kasashen waje
2017-12-04 11:05:44 cri
A ranar Lahadin da ta gabata mai gabatar da kara a kasar Masar ya mika mutane 8 da suka hada da jami'an 'yan sandan filin jirgin kasar 3 wadanda ake zarginsu da laifin safarar kudaden kasashen waje sama da dalar Amurka miliyan 113 zuwa kasashe ketare, kamfanin dillancin labaran kasar, MENA ya rawaito labarin.

Jami'an 'yan sandan 3 suna aiki ne a filin jirgin saman kasa da kasa na Cairo, da wasu mutane biyar, ana zarginsu ne da laifin karba da kuma bayar da cin hanci domin samun damar haurewa da kudaden zuwa kasashen waje ta hanyar amfani da jami'an kwastam dake aikin bincike a filin jirgin saman kasar ta Masar.

A 'yan shekarun da suka gabata, kasar Masar ta sha kaddamar da shirye shirye na yaki da rashawa, wanda ya yi sanadiyyar kamawa da kuma garkame jami'an gwamnatin kasar masu yawa da wasu manyan ma'aikatan gwamnatin kasar, lamarin da ya baiwa kasar damar kwato makudan kudade. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China