in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Masar ya gana da ministan tsaro dana cikin gidan kasar game da harin Sinai
2017-12-21 11:09:44 cri
Mai magana da yawun shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi, ya sanar da cewa, shugaban ya yi wata ganawa da ministan tsaro dana harkokin cikin gidan kasar a ranar Laraba, kwana guda bayan ziyarar da suka kai arewacin birnin Arish na yankin Sinai inda aka kaddamar da harin ta'addanci wanda yayi sanadiyyar hallakar wani jami'i guda.

A ranar Talata ne, aka kaddamar da harin bom a filin jirgin saman Arish inda ya hallaka wani jami'i guda tare da jikkatar wasu mutane biyu, harin ya dan lalata jikin wani jirgin helikwaftan a lokacin ziyarar da ministan tsaron kasar Sedqi Sobhi dana cikin gidan Masar Magdy Abdel-Ghaffar suka kai filin jirgin saman, wadanda suka koma birnin Alkahira da yammaci

Kakakin shugaban kasar Bassam Rady, ya bayyana cewa, a lokacin ganawa tasu, shugaban kasar ya karbi rahoto daga wajen ministocin biyu game da yanayin tsaro da ake ciki a arewacin Sinai, da irin matakan da aka dauka domin yaki da ta'addanci, kana da irin matakan da aka dauka don tabbatar da tsaro da zaman lumana a yankin.

Taron ganawar ya hada da shugaban ma'aikatan kasar da babban jami'in tattara bayanan sirri na kasar da kuma shugabannin hukumomin tattara bayanan sirri na sojojin kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China