in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Sisi na samun karbuwa game da bukatar sake tsayawa takara
2017-12-25 10:26:53 cri
Masu rajin shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi ya tsaya takara a zaben shekara mai zuwa, sun ce sun samu sa hannun mutane da yawan su ya kai sama da miliyan 12, wadanda ke marawa wannan kuduri nasu baya.

Da yake tabbatar da hakan, jagoran tafiyar, kuma shugaban jam'iyyar Nation's Future Party a kasar Mohamed al-Garhy, ya bayyanawa wani taron 'yan jaridu cewa, kawo yanzu sun riga sun tattara sanya hannu na al'ummar kasar 12,132,640 tsakanin watan Satumbar da ya gabata zuwa yanzu.

Mr. Al-Garhy, ya kara da cewa, babban muradin su shi ne tabbatar da nasarar shugaban mai ci yayin babban zaben kasar dake tafe, duba da yadda shugaban na Masar ya jajirce, wajen dakile mummunan yanayin siyasa da ya aukawa kasashen larabawa mai cike da tashe tashen hankula, musamman kasashen Syria, da Libya da kuma Yemen.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China