in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutanen birnin Tehran sun taru don nuna adawa da tashin hankali a kasar
2018-01-06 13:20:35 cri
Jiya Jumma'a, mutanen birnin Tehran sun taru domin nuna goyon baya ga gwamnatin kasar Iran wajen yaki da masu neman haddasa tashin hankali a kasar, da kuma nuna adawa ga gwamnatocin kasashen ketare wadanda suke son yin katsalandan a harkokin cikin gidan kasar ta Iran.

Kwanan baya, an yi zanga-zanga a birane da dama a kasar Iran, domin nuna adawa da karuwar farashin kayayyaki a kasar da wasu batutuwan dake shafar wahalar zaman rayuwar al'ummomin kasa ta Iran.

Haka kuma, bisa labarin da aka samu daga kafar watsa labarai mallakar gwamnatin kasar Iran, an ce, zanga-zanga a biranen kasar sun haddasa tashe-tashen hankula a wasu wurare. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China