Netanyahu ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa, zargin da ake yiwa kasar Isra'ila na cewa, tana da nasaba da zanga-zangar da aka yi a kasar Iran kuskure ne.
Bisa labarin da kafofin watsa labaru na kasar Isra'ila suka bayar a ranar 1 ga wannan wata, an ce, shugaban kasar Iran Hassan Rouhani ya zargi kasar Amurka da Isra'ila da suka sa kaimi ga yin zanga-zanga a kasar Iran a gun wani taro. (Zainab)