in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana goyon bayan yarjejeniyar daidaita batun nukiliyar kasar Iran
2017-12-14 13:22:54 cri
Kasashe 6 da suka shiga a dama da su a kokarin daidaita batun nukiliyar kasar Iran, da suka hada da kasashen Amurka, Birtaniya, Faransa, Rasha, Sin, da Jamus, sun gudanar da taro na 10 na majalisar hadin gwiwa mai kula da batun aiwatar da yarjejeniyar batun nukiliyar kasar Iran, a birnin Viena na kasar Austria, a jiya Laraba, tare da bangaren kasar Iran.

Darektan sashi mai kula da aikin soja da harkar tsaro a ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin mista Wang Qun, ya jagoranci wata tawagar jami'an kasar Sin zuwa taron.

A jawabin sa, mista Wang ya jaddada matsayin da kasar Sin ta dauka na goyon bayan yarjejeniyar da aka kulla kan batun nukiliyar kasar Iran. A ganin kasar Sin, yadda ake kokarin aiwatar da yarjejeniyar, yana da ma'ana sosai ga yunkurin hana bazuwar makaman kare dangi, da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a gabas ta tsakiya, don haka ya dace da moriyar bai daya ta gamayyar kasa da kasa.

A cewar jami'in na kasar Sin, kamata ya yi, kasashe 6 masu ruwa da tsaki, gami da kasar ta Iran, su ci gaba da kokarin cika alkawuran da suka yi, na tabbatar da matsayin yarjejeniyar. Haka zalika, ana bukatar su tabbatar da amincewar juna bisa kokarin gudanar da yarjejeniyar da aka kulla, gami da shawo kan sabanin ra'ayin da aka samu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China