in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a tsara manufar yin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a sabon zamani a taron koli na FOCAC na shekarar 2018
2018-01-02 19:30:45 cri

Yau Talata 2 ga wata, Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana a yayin taron manema labaru cewa, za a gudanar da taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka, wato FOCAC a nan kasar Sin, inda shugabannin Sin da Afirka za su taru a nan Beijing domin tattauna manufofin yin hadin gwiwa da sada zumunta a tsakanin bangarorin 2, da tsara yadda za a inganta hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka a sabon zamani, a kokarin tabbatar da samun nasara da bunkasuwa tare matuka.

A ranar 1 ga wata ne, shugaba Xi Jinping na kasar Sin da takwaransa na kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma suka aikawa juna sakon murnar cika shekaru 20 da kulla huldar diplomasiyya a tsakanin kasashen 2. A cikin sakonsa, shugaba Xi ya sanar da cewa, kasar Sin za ta shirya taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka a bana. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China