in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar 'yan kasuwa masu zaman kansu na Sin da Afirka na son raya harkar cinikayya tsakanin bangarorin 2
2017-12-05 19:16:17 cri
Shugaban majalisar kungiyar 'yan kasuwa masu zaman kansu ta Sin da Afirka Wang Licheng, ya bayyana a jiya Litinin cewa, za a gudanar da taron ministoci karo na 7, karkashin laimar dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka a shekarar 2018 a nan kasar Sin, inda kungiyar za ta yi amfani da wannan dama, don sa kaimi ga ayyukan zuba jari, da cinikayya a tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka.

Jami'in ya fadi haka ne a wajen taron hada hadar zuba jari, da raya tattalin arziki a fannin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, da shawarar "Ziri Daya da Hanya Daya", wanda ya gudana jiya a nan birnin Beijing. Cikin jawabin da ya gabatar wajen taron, Wang ya ce, kungiyar 'yan kasuwa masu zaman kansu ta Sin da Afirka, za ta hada kai tare da sauran hukumomi na kasar Sin, domin gudanar da wasu ayyuka na binciken yanayin kasuwanni a kasashen Afirka.

Sa'an nan kungiyar za ta taimakawa kamfanonin hada-hadar kudi na kasar Sin, domin su kara zuba jari a nahiyar Afirka, musamman ma a yankuna na masana'antu da kasar Sin ta gina wa kasashen Afirka. Har ila yau, kungiyar za ta kara kafa cibiyoyin horaswa a wasu kasashen dake nahiyar Afirka, don samun karin ma'aikata masu kwarewa. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China