in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya taya murnar gudanar da taron masu shiga-tsakani kan sakamakon taron kolin Johannesburg na FOCAC
2016-07-29 16:12:23 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika sakon taya murnar gudanar da taron masu shiga-tsakani kan sakamakon taron kolin Johannesburg na FOCAC a yau Juma'a 29 ga wata a nan birnin Beijing.

Xi Jinping ya yi nuni da cewa, wannan taro muhimmin mataki ne da bangarorin Sin da Afirka suka dauka, wajen sa kaimi ga aiwatar da sakamakon taron kolin Johannesburg na FOCAC, kana yana taimakawa wajen raya hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka. Gudanar wannan taro a cewar shugaba Xi ya shaidawa kasashen duniya cewa, Sin da Afirka na bunkasa hadin gwiwa, da samun moriyar juna duk da sauyin yanayin duniya da ake fuskantar. Kaza lika Sin na ci gaba da nuna goyon baya ga sha'anin shimfida zaman lafiya, da samun bunkasuwar nahiyar Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China