in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi: ana kokarin bullo da sabon tsarin hadin gwiwar moriyar juna tsakanin Sin da Afirka
2016-07-29 20:23:40 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyanawa 'yan jarida yayin da yake halartar taron masu shiga-tsakani kan sakamakon taron kolin Johannesburg na FOCAC yau a nan birnin Beijing cewa, taron na wannan karo ya zarce yadda aka zata a baya, ministoci da manyan jami'ai fiye da 100 daga kasashen Afirka ne suka halarci taron, wanda ya kasance gagarumin taro na hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka. Wannan ya shaida cewa, sabon tunanin hadin gwiwar Sin da Afirka musamman shirye-shirye 10 na hadin gwiwa tsakanin sassan biyu da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a gun taron kolin Johannesburg na FOCAC sun dace da bukatun kasashen Afirka, wadanda suka samu karbuwa sosai a kasashen Afirka. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China