in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Tanzania yana sa ran gudanar da taron FOCAC karo na 7
2017-11-16 16:29:21 cri
Jakadan kasar Tanzania Mbelwa Kairuki ya bayyana a jiya Laraba cewa, ana sa ran gudanar da taron dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka wato FOCAC karo na 7 a shekara mai zuwa, domin taimaka wa kasashen Afirka wajen warware matsalolin makamashi, da gina ababen more rayuwa da dai sauransu, yayin da kuma ake gaggauta ayyukan bunkasa masana'antu a nahiyar gaba daya.

A wannan rana, Mr. Kairuki ya ba da jawabi mai taken "Hadin gwiwar Sin da Afirka: yadda ake fata da kuma yadda ake aiwatarwa" a yayin taron tattalin arziki da sha'anin kudi na Caixin da aka yi a birnin Beijing. Ya ce, a halin yanzu, ana samar da wutar lantarki ga yankuna kashi 38 bisa dari a fadin nahiyar Afirka, yayin da ake samar da hidimar amfani da yanar gizo da ba ta wuce kashi 10 bisa dari a nahiyar ba, lamarin da ke haifar da ja bayan bunkasuwar harkokin masana'antu a Afirka.

Hakan a cewar sa shi ne dalilin fatansa, na ganin za a mai da hankali kan wadannan batutuwa a yayin taron FOCAC karo na 7, domin taimakawa kasashen nahiyar wajen gaggauta yunkurin raya harkokin masana'antu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China