in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi ya gana da ministocin harkokin waje 6 masu halartar taron masu shiga-tsakani kan sakamakon taron kolin Johannesburg na FOCAC
2016-07-30 12:38:36 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da ministocin harkokin waje 6 masu halartar taron masu shiga-tsakani kan sakamakon taron kolin Johannesburg na FOCAC a jiya Juma'a 29 ga wata a nan birnin Beijing, wadanda suka hada da ministan harkokin wajen kasar Afirka ta Kudu Maite Nkoana-Mashabane, da na kasar Gabon Emmanuel Issoze-Ngondet, da na kasar Benin Aurélien AGBENONCI, da na kasar Djibouti Mahamoud Ali Youssouf, da na kasar Sudan ta Kudu Deng Alor Kol da kuma ministan harkokin yankin Maghreb, kungiyar AU da kungiyar LAS na ma'aikatar harkokin wajen kasar Algeria Abdelkader Messahel, inda Wang Yi ya yi musayar ra'ayoyi tare da su kan batutuwan da suka shafi dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen da kuma batutuwan da suke kulawa tare.

Wang Yi ya bayyana cewa, sabon tunani da sabbin matakai da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a gun taron kolin Johannesburg na FOCAC sun canja zuwa sakamakon amfanawa jama'ar Sin da Afirka da yawansu ya kai biliyan 2 da miliyan 400. Sin ta nuna goyon baya ga kasashen Afirka da su zabi hanyoyin samun bunkasuwa masu dacewa da yanayinsu, kana tana son yin kokari tare da kasashen Afirka wajen kara yin imani da juna a fannin siyasa da kirkiro hanyoyin hadin gwiwa na samun moriyar juna, ta haka za a iya taimakawa kasashen Afirka wajen inganta karfinsu na samun ci gaba da kansu da kuma samun zaman lafiya da bunkasuwa mai dorewa.

Bangaren Afirka ya nuna yabo ga kasar Sin domin ta yi kira da a gudanar da taron masu shiga-tsakani na taron kolin Johannesburg na FOCAC, kana sun nuna gamsuwa ga aikin aiwatar da shirye-shirye 10 na hadin gwiwar Sin da Afirka. Ministocin kasashen Afirka sun nuna yabo ga raya dangantakar dake tsakaninsa da kasar Sin, suna son yin kokari tare da kasar Sin wajen zurfafa hadin gwiwar samun moriyar juna da sada zumunta, da inganta dangantakarsu zuwa wani sabon matsayi. Kana ministocin sun nuna goyon baya ga matsayin Sin kan batun tekun kudancin kasar Sin, suna son yin hadin gwiwa tare da kasar Sin don tabbatar da samun moriyar juna. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China