Haka kuma, ya ce, ma'aikatan 6 da suka hada da 'yan kasar Sudan ta Kudu guda 5 da na kasar waje guda 1, dake aiki a wasu hukumomin ba da agaji a kasar, na bulaguro ne a kan hanyar Raja zuwa Wau dake yammacin kasar a lokacin da suka bata.
Sanarwar ta kuma mika godiya matuka ga bangarori daban daban da suka taimaka wajen dawo da ma'aikatan agajin 6 lami lafiya, haka kuma, ana fatan bangarorin kasar Sudan ta Kudu da abin ya shafa za su dukufa wajen kare lafiyar ma'aikatan agajin MDD a lokacin da suke kokarin samar da taimakon jin kai ga al'ummomin kasar. (Maryam)