in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi kira da a gaggauta sa kaimi kan samun sulhuntawa ta fuskar siyasa a Sudan ta Kudu
2017-07-21 15:55:10 cri

A jiya ne, Liu Jieyi, zaunannen wakilin kasar Sin da ke MDD ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu kasar Sudan ta Kudu tana cikin wani hali mai sarkakkiya. Abin da ya dace a yi yanzu shi ne ci gaba da gaggauta kara sulhuntawa a kasar ta Sudan ta Kudu ta fuskar siyasa tare da samar da kwanciyar hankali a kasar.

A wannan rana, kwamitin sulhu na MDD ya kira wani taro domin nazarin halin da ake ciki a Sudan ta Kudu. A cikin jawabinsa, Liu Jieyi ya bayyana fatansa na ganin kungiyoyin shiyya-shiyya sun ci gaba da tuntubar gwamnatin Sudan ta Kudu, tare da bayyana ra'ayoyinsu da murya daya, a kokarin yin hadin gwiwa ta fuskar siyasa. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China