Jiya Alhamis mataimakin babban sakataren MDD mai kula da harkokin kiyaye zaman lafiya mista El-Ghassim Wane ya sanar wa kwamitin sulhu na MDD game da halin da ake ciki a kasar Sudan ta Kudu, inda ya sake yin kira ga shugabannin sassa daban daban na Sudan ta Kudu da su sa aya ga rikicin da ke tsakaninsu, su kuma koma kan teburin shawarwari, a kokarin samun zaman lafiya har abada. (Tasallah Yuan)