in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyya mai mulkin kasar Afrika ta kudu ta zabi wadanda za su yi takarar manyan mukamanta
2017-12-18 10:37:51 cri
Jam'iyyar ANC mai mulki a kasar Afrika ta Kudu, ta zabi wadanda za su tsaya takarar manyan mukaman da za su jagorance ta cikin shekaru 5 masu zuwa.

Wannan ya biyo bayan karewar wa'adin wadanda aka zaba shekaru 5 da suka wuce, ciki har da Shugaban Jam'iyyar kuma shugaban kasa Jacob Zuma. An zabi wandanda za su yi takarar ne yayin babban taron Jam'iyyar ANC karo na 54 dake gudana a birnin Johannesburg.

Jam'iyyar ta zabi mataimakin shugaban kasar Cyril Ramaphosa da tsohuwar shugabar hukumar kula da Tarayyar Afrika Nkosazana Dlamini-Zuma, a matsayin wadanda za su yi takarar shugabancinta. Rassan jam'iyyar 1,469 daga larduna 6 na kasar ne suka zabi Cyril Ramaphosa, yayin da rassa 1,094 daga larduna 6 suka zabi Nkosazana Zuma.

An kuma zabi David Mabuza da Lindiwe Sisulu a matsayin wadanda za su takarar mukamin mataimakin shugaban Jam'iyya.

Ana sa ran sanar da sakamakon zaben a yau Litinin, kuma ba za a bayyanawa kafafen yadda labarai tsarin zaben ba.

Taron zai kuma zabi mambobin majalisar zartarwar jam'iyyar 80. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China