in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a zabi sabon shugaban ANC a babban taron wakilan jam'iyyar
2017-12-17 12:34:13 cri
A jiya Asabar a Johannesburg, an bude babban taron wakilai karo na 54 na jam'iyyar ANC, wato jam'iyyar dake rike da ragamar mulkin kasar Afirka ta kudu. A yayin taron wanda za a shafe kwanaki 5 ana yinsa, za a zabi sabbin shugabannin jam'iyyar.

Shugaban jam'iyyar ANC na yanzu, kuma shugaban kasar Afirka ta kudu, Jacob Zuma ya bayar da rahoto kan yadda ya gudanar da ayyukansa, inda ya bayyana cewa, yanzu kasarsa na fuskantar tabarbarewar tattalin arziki, don haka akwai bukatar kawar da talauci, da kyautata rashin daidaito, da kuma kara samar da guraban ayyukan yi ga jama'ar kasar.

Baya ga haka, Zuma ya ce, ko da yake jam'iyyar ANC na fuskantar kalubaloli da dama, amma tana samun amincewa daga wajen yawancin jama'ar kasar. A cewarsa, dole ne jam'iyyar ta bada jagoranci wajen neman hanyar warware matsalolin da kasar ke fuskanta.

An yi hasashen cewa, za a zabi sabon shugaban jam'iyyar ta ANC ne a safiyar ranar 17 ga wata bisa agogon wurin, don maye gurbin shugaban na yanzu Jacob Zuma, amma shugaba Zuman zai ci gaba da zama a kujerar shugaban kasar Afirka ta kudu har zuwa lokacin babban zaben kasar a shekarar 2019. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China