Kamar yadda MDD ta tsara, an shirya yin shawarwari tsakanin wakilan gwamnatin kasar Syria da na kungiyar adawa a karshen makon da ya gabata. Haka kuma wakilan gwamnatin kasar sun koma birnin Damascus domin kara tattaunawa da jami'an gwamnati kan wannan batu.
Kaza lika, bisa sabon shirin MDD, za a tsawaita taron shawarwarin neman sulhu kan batun Syria zuwa ranar 15 ga watan nan da muke ciki. (Maryam)