Sanarwar ta ce, wannan gudummawa, wani bangare ne na tan dubu 5,404 na shinkafa da kasar Sin ta yi alkawarin bayarwa nan gaba.
Mahukuntan Kasar Sin na aiki kafada da kafada da bangaren kasar Syria don tabbatar da cewa, shimkafar da aka bayar ya shiga hannun al'ummar Syria ba tare da wani bata lokaci ba.
Da ya ke karbar gudummawar, gwamnan yankin Latakia Ibrahim Khudr Salem, ya bayyana godiya da tallafin kayan abincin da kasar Sin ta samar musu.
A jiyan ne dai wata tawaga daga ofishin jakadancin kasar Sin dake Damascus ta ziyarci tashar jiragen ruwa dake birnin Latakia a yankin arewa maso yammacin kasar ta Syria domin mika kashin farko na shinkafar.(Ibrahim)