in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilan gwamnatin Syria za su halarci taron neman sulhu na Geneva
2017-11-29 11:11:03 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Syria ta ce, tawagar wakilan gwamnatin kasar za ta isa birnin Geneva na kasar Switzerland a yau Laraba, domin halartar sabon zagayen taron neman sulhu kan rikicin kasar.

Rahotanni sun ce, gwanmatin kasar ta tsai da kudurin ne bayan ta tattauna da bangaren Rasha, inda kuma aka ba zaunannen wakilin kasar Syria a MDD Bashar al-Jaafari jagorancin tawagar wakilan.

A nasa bangare kuma, manzon musamman na babban magatakardan MDD dake kula da batun Syria Staffan de Mistura, ya ce, ya riga ya samu labarin cewa, wakilan gwamnatin Syria za su halarci taron a yau Laraba 29 ga wata.

Bayan ganawarsa da tawagar wakilan jam'iyyun adawa da gwamnatin Syria, Mr. Mistura ya ce, mai yiyuwa ne, wakilan gwamnatin Syria da wakilan jam'iyyun adawa su hau teburin sulhu kai tsaye a karo na farko yayin taron. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China