in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rantsar da sabbin 'yan majalisar ministocin Zimbabwe
2017-12-05 10:12:19 cri
Jiya Litinin, aka yi bikin rantsar da sabbin ministocin kasar Zimbabwe a birnin Harare, fadar mulkin kasar. A jawabinsa yayin bikin, shugaban kasar Emmerson Mnangagwa ya bayyana cewa, babban nauyin dake wuyan sabuwar majalisar ministocin kasar shi ne, kokarin raya tattalin arzikin kasar.

Haka kuma, ya bayyana wa kafofin watsa labarai cewa, sabuwar majalisar ministocin ta wannan karo za ta kammala wa'adin aikinta bayan babban zaben da za a yi a shekara mai zuwa, lamarin da ya nuna cewa, wa'adin aikinta ya wuce watanni shida. Sa'an nan, ya yi kira ga al'ummomin kasar da su nuna tabbaci ga sabuwar gwamnatin kasar, gwamnatin kasar za ta hada kai da dukkanin al'ummomin kasar wajen raya tattalin arziki da kuma samar da karin guraben ayyukan yi. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China