in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sabon Shugaban Zimbabwe ya rushe majalisar zartaswar kasar
2017-11-28 09:54:32 cri
Sabon shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, ya rushe majalisar Zartaswar kasar, inda ya ce yana shirin samar da sabbin ministoci.

Sanarwar da sakataren shugaban kasar Misheck Sibanda ya fitar, ta ce Shugaba Emmerson Mnangagwa ya nada Patrick Chinamasa a matsayin mai rikon mukamin ministan Kudi yayin da ya nada Simbarashe Mumbengegwi a matsayin ministan harkokin waje, domin bada damar gudanar da ayyuka ba tare da tangarda ba a muhimman ma'aikatun gwamnatin har zuwa lokacin da za a nada sabbin ministoci.

A baya, ministocin biyu sun taba rike ma'aikatun, kafin tsohon shugaban kasar Robert Mugabe ya sauya musu a watan Oktoban, biyo bayan tangade da rairaya da ya yi ga majalisar zartaswar.

Sanarwar ta kara da cewa, a yau Talata ne Shugaba Mnangagwa zai gana da dukkan manyan sakatarorin gwamnati.

An rantsar da Emmerson Mnangagwa matsayin shugaban kasar ne a ranar Jumma'a da ta gabata, bayan tsohon shugaba Robert Mugabe ya yi murabus biyo bayan matsin lamba da ya fuskanta daga sojoji da al'ummar kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China