Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Geng Shuang, ya bayyana yau Talata cewa, bisa goron gayyatar da gwamnatin kasar Zimbabwe ta ba shi, mai taimakawa ministan harkokin wajen kasar Sin, Chen Xiaodong, zai ziyarci Zimbabwe daga gobe Laraba zuwa jibi Alhamis.
Geng Shuang ya ce, akwai dadadden zumunci tsakanin Sin da Zimbabwe, kuma an cimma tudun-dafawa a hadin-gwiwar dake tsakaninsu. Kasar Sin na fatan ci gaba da hada kai tare da Zimbabwe, domin kara raya huldar dake tsakaninsu.(Murtala Zhang)