in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin ya bayyana ra'ayin kasar kan rantsar da sabon shugaba a Zimbabwe
2017-11-25 13:33:44 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana ra'ayin kasar Sin game da rantsar da sabon shugaban Zimbabwe Emmerson Mnangagwa.

Geng Shuang ya ce da yake taya Emmerson Mnangagwa murnar kama aiki, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya ce kasar Sin da Zimbabwe abokan arziki juna ne cikin shekaru da dama da suka gabata, inda ya ce kasashen biyu za su ci gaba da raya dangantakar abota dake tsakaninsu.

Ya kara a cewa, Kasar Sin tana mai da hankali sosai kan zumuncin dake tsakaninta da Zimbabwe, kuma tana son karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu ta fuskoki daban daban, domin kara tallafawa al'ummominsu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China