Da yake jawabi a jiya Talata ta kafar yada labaran kasar ZBC, Emmerson Mnangagwa, ya ce ramuwar gayya ba ta daga cikin dabi'un al'ummar kasar.
Ya ce yayin da al'amura ke ci gaba da wakana, yana bukatar al'umma su kasance masu hakuri su kuma kauracewa duk wani nau'i na daukar fansa. Inda ya kuma yi kira da su guji sabawa doka wajen warware rikice-rikice.
A yau Juma'a ne za a rantsar da sabon shugaban kasar, inda zai kammala sauran wa'adin mulkin tsohon shugaba Robert Mugabe, wanda ya yi murabus a ranar Talata da ta gabata bayan ya fuskanci matsin lamba daga sojoji da al'ummar kasar. (Fa'iza Mustapha)