Ranar 22 ga wata da tsakar rana, shugaban majalisar wakilan kasar Zimbabwe Jacob Mudenda ya sanar da cewa, jam'iyyar ZANU-PF da ke mulkin kasar ta tsai da kudurin gabatar da shugaban jam'iyyar kuma babban sakatarenta Emmerson Mnangagwa da ya zama sabon shugaban kasar, wanda zai maye gurbin Robert Mugabe, wanda ya yi murabus a ranar 21 ga wata. Za a gudanar da bikin rantsar da shi a ranar 24 ga wata a birnin Harare, babban birnin kasar. (Tasallah)