in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Emmerson Mnangagwa ya yi rantsuwar kama aiki
2017-11-24 19:35:09 cri
An rantsar da Emmerson Mnangagwa a matsayin sabon shugaban kasar Zimbabwe a yau Jumma'ar nan. Dan shekaru 75 da haihuwa, Mnangagwa ya sha rantsuwa a matsayin shugaban Zimbabwe na biyu a tarihi, yayin kasaitaccen bikin da ya samu halartar dubban 'yan kasar, da jagororin 'yan adawar kasar, da kuma baki daga kasashen ketare.

Shugaba Mnangagwa ya maye gurbin Robert Mugabe, wanda ya yi murabus daga jagorancin kasar sakamakon matsin lamba da ya sha, bayan shafe shekaru 37 yana jagorancin Zimbabwe.

Tsohon shugaban kasar Robert Mugabe, ya jagoranci Zimbabwe tun daga shekara ta 1980, bayan da kasar ta samu 'yancin kai daga Turawan mulkin mallaka.

Yayin rantsuwar kama aikin wadda babban jojin kasar Luke Malaba ya jagoranta, Mnangagwa ya alkawarta biyayya ga kundin tsarin mulkin kasarsa, da kuma kare hakkokin al'ummar Zimbabwe. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China