Jakadan kasar Sin mai kula da taron dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin kasar Sin da kasashen Larabawa Li Chengwen, ya ziyarci kasar Sudan daga ranar 20 zuwa 22 ga watan nan da muke ciki, inda ya gana da wasu manyan jami'an kasar.
Bangarorin 2 sun yi musayar ra'ayoyi dangane da aikin shirya taron ministoci karo na 8, na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Larabawa, da huldar da ke tsakanin Sin da Sudan, da ma wasu al'amuran shiyya-shiyya. (Tasallah Yuan)