A yau Litinin ne babbar kotun kasar Kenya, ta amincewa da sakamakon zaben shugaban kasar da aka sake yi a ranar 26 ga watan jiya, inda dan takarar jam'iyyar Jubilee, kuma shugaba mai ci Uhuru Kenyatta ya lashe zaben.
Dukkan alkalai a babbar kotun kasar sun amince da cewa, karar da aka gabatar dangane da sakamakon zaben shugaban kasar da aka sake gudanar a ranar 26 ga watan jiya, ba ta da isassun shaidu, don haka babbar kotun ta yi watsi da karar. (Tasallah Yuan)