in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar AU ta jinjinawa sakamakon zaben Kenya
2017-11-01 10:26:28 cri
Masu sa ido na kungiyar hadin kan Afirka AU a zaben kasar Kenya da aka sake, sun yi na'am da sakamakon zaben, suna masu kira ga masu ruwa da tsaki a siyasar kasar da su tattauna da juna, ko a kai ga kawo karshen rarrabuwar kai tsakanin al'ummar kasar.

Masu sa idon dai sun bayyana zaben wanda bai samu yawan masu kada kuri'u ba, a matsayin wanda ya dace da tanaje tanajen kundin tsarin mulkin kasar Kenya.

Rahotanni sun bayyana cewa, rashin kyawun yanayi, da kuma tarzoma a wasu yankuna da ke da yawan 'yan adawa a kasar sun gurgunta zaben a wasu sassa.

Tsohon shugaban kasar Kenya Thabo Mbeki ne ya jagoranci tawagar AU don gani yadda zaben ya wakana, duk da cewa 'yan adawa sun kauracewa shiga a dama da su a zaben karo na biyu.

Da yake karin haske game da zaben, Mr. Mbeki, ya ce AU ta maida hankali ne katsokan ga tsarin gudanar zaben, ciki hadda hada sakamako daga runfunan zaben zuwa kirga alkaluman zaben. A hannu guda ya bayyana damuwa game da yadda jami'an zaben suka fuskanci tsangwama a wasu sassan da 'yan adawa ke da karfi.

AU dai ta tura jami'an sa ido zuwa gundumomi 20 na kasar Kenya. A ranar Litinin kuma hukumar zaben kasar ta ayyana shugaban kasar mai ci Uhuru Kenyatta, a matsayin wanda ya lashe zaben da aka kammala ranar 26 ga watan oktoba, da yawan kuri'u miliyan 7.48, kimanin kaso 98.26 bisa dari na jimillar wadanda suka cancanci kada kuri'u mutum miliyan 7.61. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China