in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatan jinya a Kenya sun janye yajin aikin da suka shafe watanni 5 su na yi
2017-11-03 11:16:12 cri
Ma'aikatan lafiya a Kenya, sun janye yajin aikin da suka shafe watanni 5 su na yi a jiya Alhamis, bayan sun cimma yarjejeniya da majalisar Gwamnoni ta kasar.

Sakatare Janar na Kungiyar ma'aikatan jinya ta kasar Seth Panyako, ya ce za a fara aiwatar da kunshin yarjejeniyar da aka cimma cikin kwanaki 30, ya na mai bukatar ma'aikatan su koma bakin aiki daga yau Juma'a.

Tun a watan Yunin da ya gabata ne ma'aikatan jinyar suka kauracewa wuraren aiki, saboda a cewarsu, an saba yarjejeniyar da suka cimma da Gwamnati. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China