in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya bayyana ra'ayin kasar kan kudurin da MDD ta tsai da na tsawaita takunkumin da aka sanya wa Somaliya da Eritrea
2017-11-15 13:46:07 cri
A jiya Talata ne mukadashin zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Wu Haitao, ya bayyana ra'ayin kasar Sin game da kudurin da kwamitin sulhu na MDD ya tsai da, na tsawaita takunkumin da aka kakabawa kasashen Somaliya da Eritrea.

Wu Haitao ya ce, kasar Sin na da ra'ayin cewa, ya kamata a tsai da kudurin da zai ba da taimako ga kasashen da abin ya shafa, ta yadda za su warware matsalolinsu cikin hadin gwiwa. A sa'i daya kuma, za a iya yin gyare-gyare kan kudurin bisa yanayin da ake ciki.

Mambobin kwamitin suna da bambancin ra'ayoyi kan kuduri mai lamba 2385, wanda kwamitin ya zartas, lamarin da ya nuna cewa, ya dace a kyautata kudurin, wanda hakan ne ya sanya kasar Sin ta janye jiki daga gare shi. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China