in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Antonio Guterres ya bukaci kwamitin tsaron MDD ya tallafawa dakarun yankin Sahel
2017-10-31 10:10:55 cri
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya yi kira ga kwamitin tsaron MDD, da ya dauki matakai mafiya dacewa, wajen agazawa dakarun sojin kasashen dake yankin Sahel na yammacin Afirka.

Guterres wanda ya yi wannan tsokaci ne, yayin taron muharawa na ministocin kwamitin tsaron, ya ce ya dace kwamitin tsaron ya yi managarcin zabi a matakan da yake dauka, duba da irin kalubale da ke fuskantar kungiyar kasashe 5 na yankin sahel a fannin tsaro.

Kasashen dai sun hada da Mali, da Nijar, da Burkina Faso, da Chadi da Mauritania, wadanda tuni suka kafa wani shiri na fuskantar matsalar yawaitar bullar kungiyoyi na masu ikirarin jihadi, wanda ke yiwa yankin barazana.

Babban magatakardar MDDr ya ce idan ba a dauki matakai da suka dace ba, sauye sauye da ake fuskanta yanzu haka, na iya haifar da tashe tashen hankula masu tsanani a yankin, da ma sauran sassan masu makwaftaka.

Mr. Guterres ya kara da cewa, tallafawa kungiyar kasashen na G5, zai kasance bangare na hadin gwiwa da zai karfafa kuzarin nahiyar Afirka a fannin tunkarar matsalar tsaro.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China