in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin gwamnatin Somaliya sun harbe dakarun Al-Shabaab biyar har lahira
2017-11-07 10:18:33 cri
Bisa labarin da aka samu daga rundunar sojan kasar Somaliya a jiya Litinin, an ce, a wannan rana, sojojin gwamnatin kasar sun aiwatar da matakan soja a jihohin Middle Shabelle da Lower Shabelle dake kudancin kasar, inda suka harbe dakarun kungiyar Al-Shabaab guda biyar da bindiga har lahira.

Haka kuma, kafofin watsa labaran wuraren sun ruwaito kalaman babban kwamandan sojojin gwamnatin kasar Abdulahi Ali Anod yana cewa, a halin yanzu, sojojin gwamnatin sun riga sun karbe ikon wurare da dama a jihohin biyu, wadanda suka taba zama karkashin ikon kungiyar Al-Shabaab. Sa'an nan, za su ci gaba da daukar matakan soja kan dakarun na kungiyar Al-Shabaab. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China