Wata sanarwa da rundunar sojan Amurka dake aiki a Afirka ta fitar jiya, ta ce sojojin Amurka sun kai farmaki ta sama kan dakarun IS dake arewa maso gabashin kasar Somaliya.
Sanarwar ta kara da cewa, har yanzu sojojin na nazarin sakamakon farmakin. Kuma za su ci gaba da kokarin yaki da ayyukan ta'addanci tare da rundunar sojan Tarayyar Afirka gami da dakarun gwamnatin kasar Somaliya. (Murtala Zhang)