in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta horas da sabbin 'yan sanda don aikin wanzar da zaman lafi a Somalia
2017-10-29 12:09:46 cri
Tawagar kiyaye zaman lafiya ta kungiyar tarayyar Afrika dake kasar Somalia wato (AMISOM), ta kammala shirin horas da wasu jami'an 'yan sanda su 13 na tsawon kwanaki 9, wadanda suka fito daga kasashen Najeriya da Saliyo.

Mataimakin kwamishinan 'yan sandan shirin AMISOM, Christine Alalo, ya bayyana cewa, sabbin jami'an 'yan sandan da aka baiwa horon, za su horas da jami'an 'yan sandan kasar Somalia ne game da kyawawan dabarun wanzar da tsaro.

A wata sanarwa da aka fitar a Mogadishu, Alalo, ya bayyana cewa, manufar shirin bada horon shi ne domin baiwa jami'an 'yan sandan na AU damar samun kwarewar gudanar da aiki kasancewar sun fara gudanar da aikinsu na wanzar da zaman lafiya na tsawon shekara guda a Somalia.

Kasashen Najeriya da Saliyo suna daga cikin kasashe 6 dake bada tallafin jami'an 'yan sandan wanzar da zaman lafiya a Somalia, sauran su ne kasashen Kenya, Ghana, Uganda da Zambiya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China