in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babu yankin dake karkashin ikon Boko Haram, in ji sojojin Najeriya
2017-09-23 13:30:55 cri
Rundunar sojan Najeriya ta bayyana a jiya Jumma'a cewa, yanzu haka babu wani yanki da ya rage karkashin ikon mayakan kungiyar Boko Haram a arewa maso gabashin kasar.

Mai magana da yawun rundunar sojojin tarayyar Najeriya, kanar Onyema Nwachukwu ya ce, an dawo da dukkanin yankunan da mayakan Boko Haram suka kwace a baya hannun sojojin gwamnatin Najeriya.

Kana, Nwachukwu ya karyata rahoton dake cewa wai har yanzu akwai kananan hukumomi 27 a jihar Borno wadanda ke hannun Boko Haram.

Ya kara da cewa, matakan soja da aka dauka na kafa rundunar yaki da Boko Haram ta Lafiya Dole, sun taka muhimmiyar rawa wajen samun galaba kan mayakan, haka kuma sun kawar da mayakan na Boko Haram daga babbar matattararsu dake dajin Sambisa gami hedikwatar da suke yada da'awar kungiyar a garin Alagarno.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China