in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNHCR ta ce rikicin Boko Haram ya raba dubban yara da iyalansu a yankin arewa maso gabashin Nijeriya
2017-09-17 13:35:28 cri
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD ta ce rikicin Boko Haram ya sanya yara sama da 20,000 na watangarari tare da raba su da iyalansu a yankin arewa maso gabashin Nijeriya.

Da take jawabi yayin wani taron yini biyu kan yadda rikicin ke shafar bambancin jinsi a birnin Yola jihar Adamawa, mataimakiyar wakilin hukumar a Nijeriya da kuma kungiyar ECOWAS Bridgette Mukanga-Eno, ta ce sama da yara 8,000 aka yi kiyasin kungiyar Boko Haram ta horar tare da yin amfani da su.

Jami'ar ta kara da cewa, sama da mata da 'yan mata 7,000 ne boko haram ta ci zarafinsu, ciki har da aurensu bisa tilas.

A cewarta, mata da 'yan mata da Boko Haram ta saki, da galibi ke da yara, za su fuskanci kalubale ba kadai na nuna musu kyama da kin mu'amala da su ba, har da cin zarafi a wasu al'ummomin.

Bridgette Eno ta shaidawa mahalarta taron cewa, rahoton cin zarafin mata a sansanoni da yankunan da suka ba 'yan gudun hijira mafaka, abu ne mai matukar tada hankali, domin akwai rahoton batutuwan cin zarafi da fyade, kuma cikin masu aikata laifin har da jami'an tsaro.

Har ila yau, ta ce baya ga take hakkin dan Adam, 'yan gudun hijira ba sa iya samun gata ta fuskar shari'a da zai taimaka musu gudanar da harkokinsu na yau da kullum. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China