in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na fatan matakin MDD zai taimaka wajen samun kwanciyar hankali da zaman lafiya a zirin Koriya
2017-09-11 20:03:10 cri

Rahotanni na cewa kasar Amurka ta tsara wani sabon daftarin doka, game da shirin sanya wa kasar Koriya ta Arewa takunkumi, sakamakon gwajin makaman nukiliya da Koriya ta Arewa ta yi karo na 6. Yanzu haka dai mahukuntan Amurka za su mika daftarin dokar ga kwamitin sulhu a Litinin din nan domin kada kuri'a.

Dangane da hakan, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya jaddada a yau Litinin cewa, kasar Sin na maraba da matakin da kwamitin sulhu zai dauka, sai dai fa dole ne matakin ya taimaka wajen tabbatar da raba zirin Koriya da makaman nukiliya, da tabbatar da wanzuwar zaman lafiya da kwanciyar hankali a zirin, da kara azama kan warware batun nukiliyar zirin cikin ruwan sanyi kuma a siyasance. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China