in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron kolin kasashen BRICS ya samar wa kasashen Afirka damammaki, in ji shugaban Guinea
2017-09-08 13:16:48 cri
Kwanan baya, shugaban karba-karba na kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU, kana shugaban kasar Guinea Alpha Conde ya halarci taron shawarwari tsakanin kasashe masu saurin bunkasuwar tattalin arziki da kasashe masu tasowa, bisa gayyatar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi masa.

A ranar 6 ga wata, shugaba Conde ya halarci taron baje koli na kasashen Sin da Larabawa da aka yi a birnin Yinchuan na kasar Sin, inda ya bayyana cewa, taron kolin kasashen BRICS ya samar wa kasashen Afirka damammaki masu kyau wajen neman ci gaba.

Ya ce, kasar Sin wadda tattalin arzikinta ke saurin bunkasa tana iya kasance abin koyi ga kasashen Afirka, ta yadda kasashen Afirka za su iya koyon darussa da fasahohin kasar Sin domin raya kansu.

A yayin ziyararsa a kasar Sin, shugaba Conde ya kuma kulla wasu yarjejeniyoyin hadin gwiwa da kasar Sin a madadin kungiyar AU da kasar Guinea. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China