A yayin taron manema labaru da aka yi a yau Talata, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya ce, kasar Afirka ta Kudu za ta shirya taron shugabannin kasashen BRICS karo na 10 a Johannesburg. Kasar Sin na son hada kai da sassa daban daban wajen mara wa Afirka ta Kudu baya wajen shirya taron, a koakrin kara ciyar da hadin gwiwar kasashen na BRICS gaba.