in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: hadin gwiwar kasashen BRICS ba ya da nufin kiyayya da wani
2017-09-05 20:27:05 cri
Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ya furta a yau Talata cewa, hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen BRICS a bayyane take, tare da burin tabbatar da moriyar juna. Wannan hadin gwiwa, a cewarsa, ba ya nufin takara ko kuma nuna kiyayya ga wani bangare ba.

A cewar Mista Geng, yayin da suke hadin gwiwa da juna, kasashen BRICS suna girmama juna, da kokarin neman ra'ayi daya. Suna kuma tattaunawa da juna a ko yaushe, don haka a cikinsu babu shugaba. Suna hadin gwiwa ne don kare muradun juna, sa'an nan suna nuna ra'ayi bai daya na kasashe masu tasowa.

Ya ce, babbar manufar hadin gwiwar BRICS ita ce "musayar ra'ayi ba tare da kiyayya da wani ba, da zama tare da juna amma babu kulla kawance". Don haka ana martaba kundin tsarin MDD, da manyan ka'idojin kasa da kasa, don neman samar da wata kungiya ta bai daya da ta shafi muradun 'yan Adam baki daya.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China