in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Kenya ya amince da sake babban zaben shugaban kasar
2017-09-02 13:30:15 cri
Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta ya bayyana a jiya Jumma'a cewa, ko da yake ra'ayinsa ya saba da hukuncin da kotun kolin kasar ta yanke wanda ya soke sakamakon babban zaben shugaban kasar, yana martaba hukuncin, shi ya sa ma zai shiga sabon babban zaben shugaban kasar da za a yi.

Haka kuma, ya yi kira ga al'ummomin kasar da su kwantar da hankulansu domin kiyaye zaman lafiyar yadda ya kamata.

A ranar 11 ga watan Agustan da ya gabata ne, hukumar zabe ta kasar Kenya, ta sanar da sakamakon babban zaben shugaban kasar da aka yi a ranar 8 ga watan na Agusta, inda ya bayyana shugaban mai ci Uhuru Kenyatta a matsayin wanda ya sake lashe zaben, bisa samun kaso 54.27 bisa dari na kuri'un da aka kada.

Sai dai dan takatar jam'iyyar adawa ta kasar NASA wato Raila Odinga, ya ki amincewa da wancan sakamako, inda ya kalubalance shi a gaban kotun kolin kasar.

A kuma jiya Juma'a ne, kotun kolin kasar ta Kenya, ta sanar da soke sakamakon zaben da aka yi a watan da ya gabata tare da ayyana shi a matsayin wanda bai yuwu ba, inda ta bukaci a sake gudanar da babban zaben cikin kwanaki 60 masu zuwa.

Rahotanni na cewa, hukuncin da kotun kolin ta yanke ya jefa damuwa a zukatan mutane dangane da yanayin siyasar kasar ta Kenya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China