in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kotun koli a Kenya ta bada umarnin sake gudanar da babban zaben kasar
2017-09-01 20:26:34 cri
Kotun kolin kasar Kenya, ta bada umarnin sake gudanar da babban zaben kasar nan da kwanaki 60 masu zuwa, bayan da babban alkalin ta David Maraga ya bayyana soke zaben kasar na ranar 8 ga watan Agusta da ya gabata.

Shugaban kasar Kenya mai ci Uhuru Kenyatta ne dai aka ayyana a matsayin wanda ya lashe zaben. To sai dai kotun kolin ta ce sakamakon da aka fitar cike yake da magudi.

Al'ummar Kenya dai sun yi dakon hukuncin kotun a 'yan kwanakin nan, tun bayan da tsagin gamayyar 'yan adawar kasar NASA wadda Raila Odinga ya yiwa takara, ya sha alwashin kalubalantar sakamakon da aka fitar.

Mr. Odinga dai ya gabatar da korafin sa na kalubalantar wannan sakamako, ciki hadda wasu shaidu dake nuna yadda aka yi aringizon kuri'u, da kutse cikin na'urorin tattara sakamakon zaben, da kuma yadda aka yi amfani da kudaden gwamnati wajen yakin neman zaben shugaban kasar mai ci.

Alkalai hudu ne dai suka goyi bayan shaidun Mr. Odinga, yayin da sauran biyu kuma suka ki amincewa da shaidun. Masana shari'a dai na ganin hukuncin kotun kolin ta Kenya, ya shiga kundin tarihi, kasancewar sa na farko a Kenya, ba kuma safai ake ganin irin sa a nahiyar Afirka ba.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China