Cikin sakon da ya aike a ranar Lahadi, Shugaba Xi Jinping ya ce ya na girmama ci gaban huldar dake tsakanin Sin da Kenya, kuma ya na fatan aiki da Shugaba Uhuru Kenyatta wajen zurfafa huldarsu domin moriyar kasashen biyu da al'ummominsu.
A ranar Juma'a da ta gabata da daddare ne aka ayyana Uhuru Kenyatta a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar Kenya, bayan ya samu kashi 54.27 na jimilar kuri'un da aka kada. (Fa'iza Mustapha)