in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban adawar kasar Kenya ya kalubalanci sakamakon zaben shugaban kasar a kotu
2017-08-17 10:51:52 cri
Madugun 'yan adawa na kasar Kenya Raila Odinga, ya sanar a ranar Laraba cewa, zai garzaya kotun kolin kasar domin neman kotun ta bi bahasin sahihancin sakamakon zaben shugaban kasar da ake takaddama kansa, inda shugaban kasar mai ci Uhuru Kenyatta, aka bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben.

Odinga, ya shedawa taron 'yan jaridu a Nairobi cewa, zai kalubalanci sakamakon zaben shugaban kasar wanda aka bayyana shi a ranar Jumma'ar da ta gabata a gaban babbar kotun kasar, sakamakon zaben dai ya nuna cewa, mista Uhuru Kenyatta shi ne ya yi nasara a zaben.

Idan za'a iya tunawa a ranar 4 ga watan Maris na shekarar 2013, kotun kolin kasar ta yi watsi da karar da madugun 'yan adawar kasar ya shigar a gabanta, bayan ta hukumar zaben kasar Kenyan ta sanar da Kenyatta a matsayin wanda ya lashe zaben, kotun ta yi ikirarin rashin samun gamsassun hujjoji daga bangaren wanda ke karar.

Odinga wanda ya fadi a zaben shugaban kasar har karo na 3 a lokutan baya, ya tabbatar da cewa, zai gabatarwa kotun kwararan hujjoji dake tabbatar da cewa an tafka magudi a zaben, bayan da aka bayyana shugaba Kenyatta a matsayin wanda ya yi nasarar lashe zaben. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China