in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Sudan ta Kudu ta yabawa tawagar likitoci masu kiyaye zaman lafiya ta 7 ta kasar Sin dake kasar Sudan ta Kudu
2017-06-25 13:39:07 cri
Gwamnatin kasar Sudan ta Kudu ta yi biki a kwanakin baya, inda ta yabawa tawagar likitoci masu kiyaye zaman lafiya ta 7 ta kasar Sin dake Wau na kasar Sudan ta Kudu domin samar da gudummawa ga sha'anin kiwon lafiya na kasar. Wannan ne karo na farko da gwamnatin Sudan ta Kudun ta yabawa tawagar likitoci na Sin bayan da aka tura ta zuwa Sudan ta Kudun.

Ministan kiwon lafiya na Sudan ta Kudu Riek Gai Kok, da jakadan Sin dake Sudan ta Kudu He Xiangdong, sun bada lambar yabo ga tawagar likitoci na Sin.

Bayan da aka tura tawagar zuwa kasar Sudan ta Kudu a watan Satumba na shekarar bara, tawagar likitoci ta 7 ta Sin ta kammala dukkan ayyukan da tawagar musamman ta MDD dake Sudan ta Kudu ta bayar, kana ta bada jinya ga fararen hula 12 da suka ji rauni a sakamakon bala'u, da yara 8 dake sansanin 'yan gudun hijirar da suka kamu da cututtuka, da mutane 3 da suka kamu da cuta mai tsanani a sansanin bisa tunanin sada zumunta a tsakanin Sin da Afirka da yada zaman lafiya, kuma ta bada gudummawa wajen bada jinya ga mutanen da suka samu raunuka a sakamakon hadarin jirgin sama a kasar, da kuma bada jinya ga wata mata mai juna biyu saboda dakatar mata da zubar jini mai tsanani bayan da ta haihu. Yawan mutanen da tawagar ta bada jinya ya zarta 400, tare da taimakawa jarirai 6. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China