in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a hada kai wajen warware matsalar Sudan ta Kudu
2017-05-13 13:59:19 cri
Ofishin kakakin MDD ya ce babban magatakardan MDD Antonio Guterres ya gana da wakilan kungiyar raya kasashen gabashin Afirka ta IGAD da ta kungiyar tarayyar kasashen Afirka AU, inda ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa da su hada gwiwa wajen warware rikicin Sudan ta Kudu.

Sanarwar da ofishin ya fitar a jiya ta ce, a ranakun 10 da 11 ga wata, wato lokacin da yake halartar taro kan Somaliya a birnin London, Mr. Guterres ya tattauna da shugaban kungiyar IGAD kuma firaministan kasar Habasha Hailemariam Dessalegn, da shugaban kasar Uganda Yoweri Museveni da kuma shugaban kwamitin kungiyar AU Moussa Faki da wasu manyan shugabannin kan halin da kasar Sudan ta Kudu take ciki a yanzu.

Kuma yayin tattaunawarsu kan wannan batu, Mr. Guterres ya nuna damuwarsa matuka, kan yanayin tsaro da yanayin jin kai a kasar, inda ya jaddada cewa, ya kamata kasashen dake yankin da gamayyar kasa da kasa, su hada hannu wajen warware matsalar, musamman ma ta hanyar dakatar da bude wuta, ta yadda za a iya samar da taimakon jin kai, da kuma ba tawagar musamman da aka tura kasar damar gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.

Har ila yau, ya yi kira da a warware matsalar a siyasance ta yadda zai samu karbuwa da amincewa tsakanin al'ummar kasar tare da kawo karshen rikicin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China