Shugabannin kungiyoyin kasa da kasa dake sa ido a zaben shugaban kasar Kenya, sun bukaci dukkan masu ruwa da tsaki a zaben kasar da su bi matakan da za su tabbatar da zaman lafiya a kasar a yayin da ake ci gaba da tattara alkaluman zaben shugaban kasar.
A wata sanarwar hadin gwiwa da tagawar masu sanya idon suka fitar, sun bukaci jam'iyyun siyasa, da 'yan takara, da magoya bayansu da su kai zuciya nesa kuma su kwantar da hankulansu a lokacin tattara sakamakon zaben shugaban kasar.(Ahmad)